Skip to content
Fitowa 32:2-4

Fitowa 32:2-4

2
Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na ’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
3
Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe ’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
4
Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options