Skip to content
Fitowa 24:15-18

Fitowa 24:15-18

15
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options