Skip to content
Fitowa 1:1-7

’Ya’yan Isra’ila sun zauna suka yawaita

Fitowa 1:1-7
1
Waɗannan su ne sunayen ’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6
Yanzu Yusuf da dukan ’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options