Afisawa 4:20-24
20
Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
21
Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
22
sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
23
A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
24
Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
Settings