Skip to content
Mai Hadishi 8:1-5

Mai Hadishi 8:1-5

1
Wa yake kama da mai hikima? Wa ya san bayanin abubuwa? Hikima takan haskaka fuskar mutum, ta kuma kawo sakin fuska.
2
Ka yi biyayya da umarnin sarki, na ce, saboda alkawarin da ka yi a gaban Allah.
3
Kada ka yi hanzarin tashi daga gaban sarki. Kada ka kāre abin da ba daidai ba, gama zai iya yin duk abin da ya ga dama.
4
Da yake maganar sarki ita ce mafificiya, wa zai iya ce masa, “Me kake yi?”
5
Duk wanda ya yi biyayya da umarninsa ba zai sami lahani ba, zuciya mai hikima kuma zai san lokacin da ya dace da kuma hanyoyin da suka fi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options