Mai Hadishi 6:1-2
1
Na ga wani mugun abu a duniya, ya kuma nawaita wa mutane ƙwarai.
2
Allah yakan ba mutum dukiya, da wadata da kuma girma, don kada yă rasa abin da ransa yake so, amma Allah bai ba shi zarafin more su ba, a maimakon haka ma sai baƙo ne yă more su. Wannan ba shi da amfani, mugun abu ne ƙwarai.