Přejít k obsahu
Maimaitawar Shari’a 32:7-10

Maimaitawar Shari’a 32:7-10

7
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan ’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan ’ya’yan Isra’ila maza.
9
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options