Maimaitawar Shari’a 32:1-4
1
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
Settings