Skip to content
Maimaitawar Shari’a 32:1-4

Maimaitawar Shari’a 32:1-4

1
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options