Skip to content
Maimaitawar Shari’a 28:1-6

Maimaitawar Shari’a 28:1-6

1
In kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuka bi dukan umarnan da na ba ku a yau, Ubangiji Allahnku zai sa ku bisa dukan al’ummai a duniya.
2
Dukan waɗannan albarku za su sauko muku, su zama naku, in kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku.
3
Za ku zama masu albarka a cikin birni, za ku kuma zama masu albarka har a ƙauye.
4
’Ya’yanku za su zama masu albarka, haka ma hatsin gonakinku da kuma ’ya’yan dabbobinku, wato, ’ya’yan shanu da ’yan tumakinku.
5
Za a albarkaci kwandonku da kwanon kwaɓan kullunku.
6
Za ku zama masu albarka sa’ad da kuka shiga, za ku kuma zama masu albarka sa’ad da kuka fita.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options