Skip to content
Maimaitawar Shari’a 23:15-18

Maimaitawar Shari’a 23:15-18

15
In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
16
Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
17
Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
18
Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options