Maimaitawar Shari’a 23:15-18
15
In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
16
Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
17
Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
18
Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
Settings