Skip to content
Maimaitawar Shari’a 15:12-14

Maimaitawar Shari’a 15:12-14

’Yantar da Bayin Ibraniyawa

12
In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka ’yantar da shi.
13
Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
14
Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.

Nazarin nassin nan

Sharhi a kan nassin, ba aya ɗaya ba

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Irmiya 34:14

    ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă ’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi ’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
    daga aya ta 12
  • Fitowa 21:2

    “In ka sayi mutumin Ibraniyawa a matsayin bawa, zai bauta maka shekara shida. Amma a shekara ta bakwai, za ka ’yantar da shi, yă tafi ’yantacce, ba tare da ya biya kome ba.
    daga aya ta 12
  • Fitowa 21:6

    dole maigidansa yă kai shi gaban alƙalai. Zai kai shi ƙofa ko madogarar ƙofa, yă huda kunnensa da basilla, sa’an nan zai zama bawansa duk tsawon kwanakinsa a duniya.
    daga aya ta 12
  • Firistoci 25:39

    “ ‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta a cikinku, ya kuma sayar da kansa gare ku, kada ku sa yă yi kamar bawa.
    daga aya ta 12
  • Firistoci 25:41

    Sa’an nan a sake shi da ’ya’yansa, yă kuma koma ga danginsa da mallakar kakanninsa.
    daga aya ta 12
  • Maimaitawar Shari’a 15:1

    A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
    daga aya ta 12
  • Yohanna 8:35

    Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada.
    daga aya ta 12
  • Yohanna 8:36

    Saboda haka in Ɗan ya ’yantar da ku, za ku ’yantu da gaske.
    daga aya ta 12
  • Irmiya 22:13

    “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
    daga aya ta 13
  • Malaki 3:5

    “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
    daga aya ta 13
  • Karin Magana 3:27

    Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
    daga aya ta 13
  • Karin Magana 3:28

    Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
    daga aya ta 13
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options