Ayyukan Manzanni 8:15-17
15
Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
16
domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
17
Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.