Ayyukan Manzanni 8:14-16
14
Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
15
Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
16
domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
Settings