Skip to content
Ayyukan Manzanni 3:21-24

Ayyukan Manzanni 3:21-24

21
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki.
22
Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
23
Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
24
“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options