Skip to content
Ayyukan Manzanni 27:33-38

Ayyukan Manzanni 27:33-38

33
Kafin gari ya waye Bulus ya roƙe su duka su ci abinci. Ya ce, “Kwana goma sha huɗu ke nan, kuna zama cikin zulumi kun kuma kasance ba abinci, ba ku ci kome ba.
34
Ina roƙonku yanzu ku ci abinci. Kuna bukatarsa don ku rayu. Ba ɗayanku da zai rasa ko gashin kansa guda ɗaya.”
35
Bayan da ya faɗi haka, sai ya ɗauki burodi ya yi godiya ga Allah a gabansu duka. Sa’an nan ya gutsuttsura ya fara ci.
36
Dukansu kuwa suka sami ƙarfafawa, suka kuma ci abinci.
37
Dukanmu a jirgin kuwa mutane 276 ne.
38
Sa’ad da suka ci iyakar abin da suke so, sai suka rage nauyin jirgin ta wurin zubar da hatsin a cikin tekun.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options