Skip to content
Ayyukan Manzanni 19:17-20

Ayyukan Manzanni 19:17-20

17
Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai.
18
Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu.
19
Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin.
20
Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options