2 Sama’ila 14:8-9
8
Sarki ya ce wa macen, “Koma gida, zan ba da umarni a madadinki.”
9
Amma macen da ta fito daga Tekowa ta ce, “Ranka yă daɗe, sarki! Bari alhakin shari’arka yă kasance a kaina da gidan mahaifina, kai sarki da gidan mulkinka, ba ku da laifi a ciki.”