1 Sama’ila 14:8-10
8
Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
9
In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
10
Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
Settings