Skip to content
1 Sama’ila 14:24-26

1 Sama’ila 14:24-26

24
A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
25
Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
26
Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options