Skip to content
1 Bitrus 2:21-24

1 Bitrus 2:21-24

21
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options