1 Sarakuna 8:10-13
10
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
Settings