1 Sarakuna 13:18-19
18
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’ ” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.