Skip to content
1 Korintiyawa 15:25-28

1 Korintiyawa 15:25-28

25
Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
26
Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.
27
Gama ya “sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” To, da aka ce an sa “kome” a ƙarƙashinsa, a fili yake cewa ba a haɗa da Allah a ciki ba, shi wannan da ya sa kome a ƙarƙashin Kiristi.
28
Sa’ad da ya yi haka, sa’an nan Ɗan kansa yă koma a ƙarƙashin shi wanda ya sa kome a ƙarƙashinsa, domin Allah yă zama kome da kome.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options