Zabura113
Listen to this chapter
0:00
0:00
1
Yabi Ubangiji. Ku yabe shi, ya ku bayin Ubangiji, ku yabi sunan Ubangiji.
2
Bari a yabi sunan Ubangiji, yanzu da har abada kuma.
3
Daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa, a yabi sunan Ubangiji.
4
Ana ɗaukaka Ubangiji a bisa dukan al’ummai, ɗaukakarsa a bisa sammai
5
Wane ne yake kamar Ubangiji Allahnmu, Wannan mai zama a kursiyi can bisa,
6
wanda yake sunkuya yă dubi sammai da duniya?
7
Yakan tā da matalauta daga ƙura yakan ɗaga mabukata daga tarin toka;
8
ya zaunar da su tare da sarakuna, tare da sarakunan mutanensu.
9
Yakan zaunar da matar da ba haihuwa a gidanta ta zama kamar mahaifiyar ’ya’ya mai farin ciki. Yabi Ubangiji.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Options
Study Note