Ru’uya ta Yohanna 21:24-26
24
Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin.
25
Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba.
26
Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin.