Skip to content
Ru’uya ta Yohanna 21:23-26

Ru’uya ta Yohanna 21:23-26

23
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, gama ɗaukakar Allah tana ba shi haske, Ɗan Ragon kuwa shi ne fitilar birnin.
24
Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin.
25
Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba.
26
Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options