Skip to content
Ru’uya ta Yohanna 20:7-9

Ru’uya ta Yohanna 20:7-9

7
Sa’ad da shekaru dubun nan suka cika, za a saki Shaiɗan daga kurkukun da yake,
8
zai kuma fito don yă ruɗi al’ummai da suke a kursuyoyi huɗu na duniya, Gog da Magog, yă tattara su don yaƙi. Yawansu kuwa ya yi kamar yashi a bakin teku.
9
Suka mamaye duk fāɗin duniya suka kuma kewaye sansanin mutanen Allah, birnin da yake ƙauna. Amma wuta ta fito daga sama ta cinye su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options