Zabura 94:7-11
7
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Settings