Skip to content
Zabura 92:7-15

Zabura 92:7-15

7
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14
Za su ci gaba da ba da ’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options