Skip to content
Zabura 81:11-16

Zabura 81:11-16

11
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options