Zabura 78:68-72
68
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Settings