Zabura 74:12-17
12
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Settings