Zabura 68:28-31
28
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin ’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Settings