Zabura 48:3-8
3
Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
4
Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
5
sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
6
Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
7
Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
8
Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. Sela
Settings