Skip to content
Zabura 37:1-6

Zabura 37:1-6

1
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options