Skip to content
Karin Magana 7:10-16

Karin Magana 7:10-16

10
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options