Karin Magana 7:1-5
1
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4
Ka faɗa wa hikima, “Ke ’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
Settings