Skip to content
Karin Magana 2:1-9

Karin Magana 2:1-9

1
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options