Karin Magana 2:1-9
1
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Settings