Karin Magana 2:1-5
1
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Settings