Skip to content
Karin Magana 12:8-14

Karin Magana 12:8-14

8
Akan yabi mutum bisa ga hikimarsa, amma mutane marasa azanci akan rena su.
9
Gara ka zama kai ba kome ba ne amma kana da bawa da ka mai da kanka kai wani ne alhali kuwa ba ka da abinci.
10
Mai adalci kan kula da bukatun dabbobinsa, amma halaye mafi kyau na mugaye su ne ƙeta.
11
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami abinci a yalwace, amma shi da yake naushin iska marar azanci ne.
12
Mugaye suna sha’awar ganimar mugayen mutane, amma saiwar masu adalci kan haɓaka.
13
Mugun mutum kan fāɗa a tarkon maganarsa ta zunubi, amma adali kan kuɓuta daga wahala.
14
Daga abubuwan da suke fitowa daga leɓunansa mutum kan cika da abubuwa masu kyau tabbatacce yadda aikin hannuwansa suke ba shi lada.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options