Skip to content
Karin Magana 11:27-31

Karin Magana 11:27-31

27
Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
28
Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
29
Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
30
’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
31
In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options