Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2
“Ku yi ƙidaya Kohatawa daga Lawiyawa, bisa ga kabilarsu da iyalansu.
3
Ku ƙidaya dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin da suka zo domin aiki a Tentin Sujada.
4
“Ga aikin Kohatawa a Tentin Sujada, kulawa da kayayyaki mafi tsarki.