Skip to content
Mattiyu 25:10-12

Mattiyu 25:10-12

10
“Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
11
“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
12
“Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options