Skip to content
Mattiyu 22:23-28

Mattiyu 22:23-28

23
A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
24
Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya.
25
A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
26
Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
27
A ƙarshe, macen ta mutu.
28
To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options