Mattiyu 13:41-43
41
Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
42
Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
43
Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”