Skip to content
Markus 4:16-19

Markus 4:16-19

16
Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
17
Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
18
Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
19
amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options