Luka 23:35-37
35
Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
36
Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
37
Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”