Skip to content
Luka 19:28-30

Luka 19:28-30

28
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
29
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
30
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options