Luka 15:14-16
14
Bayan ya ɓatar da kome, sai ga muguwar yunwa a dukan ƙasar, har ya shiga rashi.
15
Sai ya je ya sami aiki a wurin wani mutumin ƙasar, wanda ya aike shi a gonakinsa, ya yi kiwon aladu.
16
Ya yi marmarin cin dusan da aladun suke ci, amma ba wanda ya ba shi wani abu.