Yunana 4:7-8
7
Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye ’yar kuringar har ta mutu.
8
Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”